Friday, May 14, 2010

The Roaring Crowd

Umar uba jama’a
Short Story
It was Monday morning, as I prayed, bathed, had my breakfast and got dressed for the office. I had my dress for the week in y brief case. I bid farewell to my family and leave.
I stopped a bike to take me to the bus station. Suddenly, I felt I had forgotten something. I took excuse from the bike man. I rushed back into the house and my wife asked if I had forgotten something. I said, I don’t think so. I looked at her and rushed back to the waiting bike.
I was the seventh passenger, later the eighth passenger came in. A lady in her teens.
She came with an elderly man in military uniform. They discussed. He bid her farewell and left. She boarded the bus, sat next to me and we greeted.
We adjusted for her comfort as the last person on the row.
The man came back and knocked on the glass window. ‘Yes Daddy?’ she questioned. ‘You forgot anything?’ ‘No papa.’ ‘Ok He then left. The driver was then set to go, then, this man came back to speak with his daughter again. ‘please tell your mummy that I’ll be coming in the next two months.’ He waved at her as the driver pressed the gas.
At about half the journey, the conductor asked for the fare and I paid for myself and hers. Pretending we were together. She looked at me and that was when we looked at each other straight in the eyes. ‘Thank you’ she said. The conductor handed me the change.
I looked at her again and asked. ‘Was that your dad?’ ‘Yes.’ She answered and remained silent. “Are you going to school...?’ I asked in a low tone. ‘Nope, I’m going to stay with mum until my JAMB is out.’ She replied. ‘That was your father
and your mum is somewhere else?’ ‘Actually mum is late. I’m staying with his sister ‘ we became friends as we drove into town.
The town was unusual as there were less vehicles going in and out. The driver pumped up his gas to high speed, to enjoy the empty township road.
Head-on we met a group of men marching the highway. We stopped too close for a reverse.
They were holding all sorts of crude weapons. They surrounded our bus. We all began to shiver as fear engulfed us.
They opened all the bus doors and began to pull us out stabbing and machetting some of us. This lady held my hand as she was pulled out and someone from the faceless crowd smashed machete on her as she screamed for help releasing her hand off mine and falling to the ground.... Her blood splashed on my clothes staining them. I was pushed to the center of the crowd and was forced to follow the roaring crowd. This continued for about two hours before I realized we were close to the footpath into the military barrack. I skidded off to the barrack.
Close to the highway was a friend’s house. Without knocking I pushed the door, staggered in to the parlor and I fell to the ground. The woman in the house recognizes me and shouted my name. I remember looking at her and not saying a word with my eyes wide opened.
She helped me to the shower. I just turned the knob without removing my blood stained clothe or shutting the door. As the cold water ran through my body I collapsed and fainted. When I woke up I was told to have been two days in the military specialist hospital.
The End.
U. Uba jama’a.

Hausa fiction

Umar Uba

HONORABIN DA JAMA’ARSA: (1)

Ko da na taso na taso ne cikin abokai a unguwarmu kamar yadda kowanne yaro kan taso cikin tsararrakinsa. Mu dai mu bakwai ne muka dore da muka kawo lokacin da muka san ciwon kanmu.
Dayanmu ne kawai ya kasance ba shi da mata amma mu sauran har akwai mai mata uku baicin mu biyu da keda mata biyu-biyu.
A kullum muka dawo aiki ko a karken mako mu kan taru a majalisa. A nan ne za ka ji labari iri-iri, kasancewarmu kuwa kowa wurin aikinsa daban.
Mu kan dora shayi irin na buzaye a kullum. Wannan ya zama mana kamar fadi don har matanmu kan yi mana surutu a kansa, a wasu lokuta ma su kan hana mu gawayi ko a ce ba a ga bangaldin ba. Da zaran an fara shan shayin nan an soma kawo labaru ke nan da shawarwari.
Yau da kullum har soja suka ce za su ba da mulki ga ‘yan siyasa don haka aka kakkafa jam’iyyu. Dukkanmu muka farfasu a cikin jam’iyyu kowa da ra’ayinsa.

Daya daga cikin abokan nawa da baya aiki rannan sai ya kawo shawarar zai tsaya takaran kansila a unguwarmu. Nan fa muka yi masa can-cagwadi muka yi ta masa tsiya kamar ba tare muke da shi ba. A karshe dai muka amince za mu goya masa baya ko da yake muna cikin jam’iyyu daban daban.
Bayan kada kugen siyasa ‘yan takara suka fito, shima Habu ya yi rajista. A ka bugo fosta, mu ka baza ta a gari. A ka shiga ziyarce-ziyarcen yakin neman zabe. Da kafa muke tafiya zuwa kauyukan da ke cikin mazabarmu. Duk kofar gidan da muka je ra’ayinsu daban. Wasu su yi korafi. Wasu su yi fatar alhairi wasu kuma su mika kukansu na matsalolin su ko bukatunsu..
Duk tsawon zagayen da muka yi da kafa mutun daya ne,wani dattijo malam Jibo ya bamu mamaki saboda irin nasa hangen nesan ya ban-banta da sauran. Bayan mun gaisa da shi a kofar gidansa mu ka fada masa manufarmu sai ya yi mana addu’a sannan ya kama hannun Habu ya ce “ni abinda kawai nake so idan Allah Ya sa anyi nasara to duk ran da Allah ya biyo da kai ta kofar gidana ina nan bisa dakali, to ince Honorabin! Kai kuma ka dago mun hannu ka jinjina don duk wa’yanda mu ke tare dasu su san muna tare ko idan ka sayi mota in za ka wuce ka yi mun hon ko inda hali katsaya mu gaisa kawai, shi kenan abinda nake so Allah Ya bada sa a”.

Zabe ya zo mu ka yi ta gwagwarmaya ba dare ba rana har daren zabe mutane ko na ta korafi don mun cika musu fuska mu kuma ba sisi sai dadin baki. Haka nan mu ka dode kunnuwanmu, mu kayi fuska muna ta yake..
Ranar zabe a ka yi ta zurutu bamu wannan bamu waccan rumfa. A wasu rumfunan mu tarar a na ta fada a bayan fage, sai mun yi tsaye sannan mu raba. Ba wani abu ya kawo yawan fadace-fadacen ba face sauran ‘yan takaran su na ta raba kudi a layin masu zabe a sake. Sai a rika bin mata a na lika masu ‘yar N20 ko N50. haka nan ‘yan gutsatsin yaran da ke layi a ka yi ta binsu da ‘yan kudaden nan. Ko ina mutanenmu kuwa su ka yi zuru-zuru na abinci ma kusan gagaran mu ya yi..honorabin kuwa barci ya gagara tun kwana uku da suka wuce duk ya yi zuru-zuru dashi yunwa ta fara kammashi.

Yamma ta yi a ka rurrufe rumfunan zabe. Aka fara kirga kuri’u. nan fa jikin mu ya yi sanyi ganin irin kudin da sauran jam’iyyu su ka rabar, bamu cire rai zamu ci wannan zaben ba amma mun sani sai dai taimakon Allah. Mun barwa Allah mun dai tabbatar da tsare akwati.
Ko da aka fara kawo sakamako a makarantar firamare da ke unguwar tsakiya sai muka shirin watsewa domin unguwanni uku cikin goma sha dayan da ke yankin namu d asu ka fara iso wa duk mun fadi.Ana ta yi mana sowa, a ka fara nuna mu.
Ina ya Allah-babu ya Allah, sauran sakamakon mu ka yi ta samun nasara. Duk akwatin da aka kawo sai muyi masu fintinkau. Nan da nan fuskokin mu ta saki. Mu ka fara murmushi. Da dai mu ka ga alamun sa’a na garemu na amso kires na lemu a shagon da ke kusa, mu ka fara rabawa jama’ar da su ka yini da yun wa. Zuwa sha-dayan dare a ka gama kidayar a mazabarmu kuma aka tabbatar mana da nasara. Nan da nan yaranmu su ka sa kida da jarkoki, su ka shiga bin layi-layi sunaragar-gajewa. Mu kuma mu ka dunguma da jami’an zabe mu ka nufi karamar hukuma.

Bayan ‘yan kwanaki mu ka dawo da zaman majalisa sosai. Mu ka fara muhawarar zabe. Yadda muka ci kafar juna a jam’iyyance. Honorabin habu kuwa zaman majalisa ya gagareshi. A kullum idan ya fita sai tsakar dare zai dawo. Lokacin da muke kokuwar zuwa aiki kuwa shi bai tashi barci ba. Nan da nan ya samu barori.da a kwai masu yi masa wanki da guga. ‘yan aike nan da can kai har ma mai gyara masa daki a gyara masa gadonsa idan ya fita. Hutu ya samu kwarai. Matsalarsa kawai ba shi da mata. A kullun kofar gidan da honorabin ke kwana a dakin zauren yak an cika da jama’a masu neman alfarma. Manyan mutane da manyan motocinsu su kan bugo sammako don ganin hanorabin domin shine a kan kujerar kansilan ayyuka don haka duk wata kwangila sai ta bi ta hannunsa.
Tun ana daukarshi in zashi aiki a babur a sauke shi a bakin hanya ya shiga bos a ka shiga kai shi a babur har sakatariya. Cikin dare ko idan kaji karar mota to an kawo maigida ne. nan da nan girma ya samu. Wata rana kawai cikin dare sai honorabin ya shigo da wata tsaleliyar mota.
Unguwar tamu mota guda ce, ta Alhaji Ibrahim. Duk lokacin day a dumfaro gida tun daga nesa kowa ya san shine ke dawowa sabo da tsufar motar.
Muka wayi garin asabar da wannan tsaleliyar mota a kofar gida. Muka ko kewayeta muna ta murna. Nan muka yi dandazo har honorabin ya tashi barci. Bayan ya kintsa a dakinsa, ya fito kofar gida fuskar ba ko annuri wai shi alamun ya gaji. Ganin mun tsura masa ido ya dan saki fuska ya danyi murmushi. A ka gaggaisa da jama’a duk mu ka yi masa murna. Da dai muka ga babu fuska ni da kabiru sai muka tashi daga dandalin. Da ma mu ba mu saba da maula ba. don shi zai dauka duk wanda ke wurin so yake ya ba shi wani abu.

A kullum kafin honorabin ya tashi an wanke motarsa an share kofar gidan. A kwana a tashi bayan ‘yan watanni ya sayi fili gefen gari. Nan da nan a ka sa tushen gini. A daidai lokacin kuma muka ji yana neman aure. A ka sa masa rana wata uku. Cikin wannan lokacin ne a ka gama ginin gidannan. Duk unguwar babu gida irinsa. Dutse da dutse gashi ya sha ado ko gidan sarki albarka. Mu ma a garin muka samu gidan kwatance.
Lokacin buki ya zo, honorabin ya bugo kati. A ka aiko mana da na majalisa. Ranar ce Hassan ya ce “a’a, a she honorabin na sane da mu?” saura duk mu ka yi shiru. Kowa na ciki-na ciki. Tun ana saura kwana uku a ka fara toye –toye da zirga –zirga a sabon gidan honorabin ba kama hannun yaro. Cikin dare ya tattara kayansa daga dakin zauren ya tare a daya daga cikin dakunan da ke gidan. Ga kuma motarsa an sama mata gareji.

Bayan daurin aure muka yi masa murna sannan ya shaida mana akwaai walima a firamare. Ko da lokaci ya yi mu ka isa, a ka hada mu da shinkafa ta tsotse da zobo. Shi ko, ko kafarsa ba mu gani ba. Can da rana ta yi alamun faduwa ne a ke shaida mana ai ya na can a birni da amarya da manyan sabbin abokanensa suna karya kashi a wajen party.
Da ga nanne muka san annabi ya faku. Domin lallai wulakancin ya isa. Kuma ya nuna mana abin da bahaushe ke cewa “kowa ya yi sarki ya darma sa a.’’ wato habu ya zama honorabin, ya yi mota, ya yi gida. Yanzu ya yi aure ganin ba za mu tsinana masa komai ba ne ya yi mana haka?” shagargari a ka aiko mana da kalanda, a nanne muka ga irin amaryar. “Lallai honorabin ya darzo.Allah Ya bada zama lafiya” mu ka sha shayi mu ka waste. Bayan shekara uku idan ka cire dankareren gidan da honorabin ya gina sai wata rubabbiyar gada da su ka yi raba dai-dai da daankwnagilan ba bu aikin da aka tsinana a garin.gamu ko, abokanensa ragon suna ko buhun shinkafa da sallah sai dai muji ya ba wasu. “kai Allah wadan naka ya lalace.” Inji dan kwairo, bayan ya kora shayi.

Lokacin da aka fara nuna masu saura watanni shida a sake zabe sai honorabin ya fara tunanin komawa kujerarsa. Nan da nan ya fara tara taro da yara da dattawa a kauyakun. Jama’a ko suka bude baki ya yi ta antaya masu kudi. Da zaran ya tashi sukan ce “mu ci rabonmu ke nan, karken mulkin zalunci ne ya zo.”ha ka ya yi ta kasha kudi, ya na son ya yi tazarce. Mu kuwa ya yi watsin tamba dam u. mu ma da muka ga haka muka juya masa baya muka kuma daura yakarsa.
Labarin honorabin na Allah mai-maita mana ya karade gari. Duk wani motsi da yayi sai an kawo mana labrinsa mu kuma muna bi muna warware tukkan day a ke yi.. haka nan labarinsa na bariki duk ya iso garemu har ‘yammatan da yasaya wa GSM da wa’yanda ya sa a ka dauka aiki duk muna da labarin su. Irin albashinsa da kashi-mu-raba da ya ke yi da ‘yan kwangila kuwa abin ba misali. Ga dai motoci ya saya ya sa a titi. Direbobi sai hidimarsuu su ke yi,duk wani gida da aka daga za a sayar lallai zai fanshe shi. Ya sayi filaye da gonaki. Kai honorabin ya gagara.

Wata rana muna zaune a majalisa muna shan shayi sai malam jibo ya zo wucewa. Muka gaisa mu ka yimasa tayin shayi. Ya ce”kai samari, anya na sha wannan shayi na ku?’ nan da nan muka mika masa kofi guda ya tsuguna a gefe guda ya dan kurba, ya bata rai saboda baurinsa. Ya daga kai ya ce “a’a ina mutumin naku ne habu kansila? Kun san tun da na kwanta ciwo ga shi har na sami sauki na fara daddagarawa ban sa shi a ido ba.”
“a’a baba ai abin yanzu ya fi karfin mu ne, kasan kowa yayi sarki ya daramma saa.” Na ce dashi na ja baki na na yi shiru.




HONORABIN DA JAMA’ARSA 11
Zabe saura wta uku honorabin da matarsa su ka tafi aikin hajji. Bayan tashin su ne a ka sake wa gidansa fenti, a kai zubin kujeru da kafet har da sabbin kantoci. Masu aiki su ka ci su ka sha.
Bayan dawowarsu mu ka je mu ka yi masu murna. Mu ka sha rowan zam-zam. Mu ka ci dabino da bagaruwa. Ko da jirgin kaya ya iso. Honorabin ya karbo kayansa. Ya aiko mana a majalisa carbi da irin huluna nan Alhaji ya sallami dan’iska. Ran nan ya roke ni in raka shi gidan surukansa. Ya dauke ni a motarsa mu ka shiga birni mu ka yi ta yawo lungu-lungu mu na raba tsaraba. Daga turmin zani, jallabiya irin ta mata,dankwalaye wasu ma dai ni ban san ko menene a cikin ledar ba. Bayan motar nan shake ya ke da kayan. Sai da mu ka rabar sannan mu ka dawo gida. Wani abu da na yi tunani shin honorabin ya na ganin bana bukatar tsaraba ne? amma kila nawa sai da safe za a aiko mun da shi. Haka nan dai na ji tsit.

Bayan “yan kwanaki sai ranar zabe ta zo. Mu ka ce ko da wa Allah ya hadamu ba da honorabin ba?’ mu ka yi masa tuggu iya tuggu. Mu ka jawo duk samarin da malaman islamiyyoyin da ke unguwannin mu ka ba su manufa. Mu ka karanta masu ire-iren aibobin hanorabin da ba su sani ba. A nan ne su ma su ka nuna mana da ma shake su ke da shi. Mu ka sa su su bi gida-gida da sassafe su ka yi wa mata huduba.su ka kuma nuna masu alkibla.. Dama duk dalibansu ne. su ma a ka sa su a layi. Honorabin kuwa ya bude bakin aljihusa ya yi ta raba kudi kamar wani mai injin bugasu a gida. Ko da rana ta yi a ka tantance masu zabe a kasa ‘yan takara a bisa dakali, nan honorabin ya soma ganin tasku.a nan ya ga layin dan takaranmu ya masa fintinkau. Ya yi wuri-wuri da idanuwa ya ga wa’yanda suka ci masa kudi. Mu kuma mu ka yi kamar ba mu san Allah Ya yi ruwan tsirarsa ba. Haka a ka yi zabe a ka gama honorabin ya kwashi kasa. Da gari ya waye, gari ya yi tsit. Kofar gidan honorabin kuwa kamar an share. In banda barrorinsa da ‘yan gani kasheninsa. Mu kuma mu ka koma majalisa mu ka ci gaba da dangantaka. Honorabin kuwa ya dauke kafa ga kowa. A ganinsa ya tara isassar dukiya da za tai she shi rayuwa duk da iyalinsa.

Nan da wata guda za su sauka da ga karaga, sabuwar gwamnati ta hau mulki. Gashi an kada shi a zaben fidda gwani. Gaisuwa ta gagara tsakaninmu. ‘mu ka ce oho dai! Da ma ba mu ciba bare ido ya yi kunya.”
Bayan zabe,abokinmu da ke unguwar da ke ketaren dogo wanda shi ne ya ci zaben ya zo ya bi mu gida-gida ya na godiya. Da ga nan shima ya zama jiki ya na gayyatarmu, duk wani sha’ani da za shi zai tabbatar ya je da daya daga cikinmu. Ya kansa lokaci kamar karken mako ya zo shima a yi zaman majalisa da shi. A hankali shi ma mu ka ce “honorabin ko za ka yi rajista ne a majalisa?” ya sa mu cikin al’amuransa mu ka yi ta ba shi shawar-wari na gari don gabatar da ayyukan ci gaba.

Honorabin kuwa ya koma cin baro. Motocin da ya zuba a hanya su ka soma tangarda. Direbobin kowa ya yi ta kokarin yin tashi motar sannan ya kashe ta honorabin. Injunan motocin nan su ka soma bugawa dai-dai. Ko da su ka rage saura biyu rannan daya ta fadi. Da haka a ka sayar da ita don ta tayar da dayar. Ya soma sayar da filayensa sannan ya shiga rigima da ‘yan haya, kafin wata ya kare ya kan yi ta aike a karbo masa wani abu. Cikin shekara uku honorabin ya kasance saura motar da ya ke shiga kawai. Babbar gonar da ya saya a daji kuwa wadda yanzu ba ya iya noma ta sai ya bada jinginarta.
A kwana a tashi sai honorabin ya soma rasa inda za shi ya rage rana. Ya kan rasa wurin zuwa. Daga nan ya soma kewayowa zuwa majalisa. Tun muna kyararsa har dai mu ka soma sakin jiki da shi.

A wani karken mako sai honorabin ya neme mu mu uku ya ce dun Allah mu raka shi wajen mai gidansa. “yallabai an ce ya shigo gari ina so ku raka ni mu je mu yi gaisuwa.”
Na daukesu a motata mu ka isa gidan yallabai. Tun da ga nesa mu ka hango tarin motoci da babura. Ganin haka mu ka ce lallai mun yi sa a. Na aje mota da ga nesa. Mu ka shiga rububin jama’a don ganin ‘mai gida.’
Yallabai dai ya gana da wannan ,ya gana da wancan a cikin baban falonsa. Mu na hangen yadda jama’a kan sau da kai idan ya na masu bayani ta babbar tagar falon. “Allah ya sani tun da na ke jin sunansa a siyasa sai yau na ke ganinsa.” Na ce wa daya daga cikin dattawan da mu ke tare. Ko da wasu tarin jama’a su ka fita sai sarkin fada ya ce “to sai ku.” Mu ka shige katon falon nan mun fara gaisuwa ke nan, sai wasu ‘yam mata biyu su ka shigo daga kofar cikin gidan da manya-manyan farantai dauke da kwanonin abinci.. Ga alama dai ‘ya’yansa ne saboda irin kamar da su ka yi da shi. Yallabai ya yi mana maraba kuma ya nuna duk ya san jama’ar da mu ke tare da su sai nine kawai bai nuna ya sani ba.
Ya yi mana tayin abinci. Kowa ya sa hannu ya dauki kwano har da honorabin Abu. Ni kuwa na ce na koshi don haka ko ruwa ban sha ba.
Umar Uba

short story ....and he died

NAME: Umar Uba

SHORT STORY


Title… And he died.

I grew up in a matrimonial home where my father was married to three wives. I am the only son of the second wife and the second son of my father with oldest being a female … now housewife.
I am a few months older than my next-of-kin in the family of fifteen. He was the only one who doesn’t respect my age. He sometimes claimed being my senior. I always been cautioned by my mother to remain softhearted and never succumb to his aggressiveness. I headed her advice and never want to fight him at this age.
We are both married. Having more kids than him and living with our parents made it compulsory for him to see me anytime he come in.
I took interest in his two kids and made them homely and friendly. They waved and smile each time they saw me – may be just to make him happy towards me.
He hardly come home, even if he did he remained as quiet and disrespectful as possible to all, especially, to our father and the rest of his wives. This attitude kept on burning in him.
One day I was home in the morning as always. After finishing the daily chores of regards to everyone in the house, my mother told me that my brother was in his mothers’ room, he was not feeling fine. I peeped into the room and wished him well.
He began to come home often and almost spending the whole day indoors. I then asked myself, “What is keeping him home”. Days went bye. He began to sleep in his younger brothers’ room. My mother asked me another day “Have you been greeting him?” ‘Who’. I asked, “Your brother he has been home for the past few days”. She replied I then wondered again how sick he should be to allow himself to leave his family in the next village and come home and stay. His kids and wife visited him regularly. The kids at time would past the night in my house, which is the next block from the families. The wife being a working mother always slept in their one room rented apartment.
He began to loose weight and strength resisting all application. No information was communicated to me as to what sickness he was suffering from except as describe a common but deadly, incurable sickness (pile) that was being taken care of by local medication. A local physician also attends to him – I don’t known on what prescription/he received several pints of intravenal water along with extra medications. His mother and other relatives brought all sorts of local medications to aid his health.
The situation continued to worsen. He hardly could walk without a stick. He lost weight. He hardly could say exactly what he wanted to say each time he attempted speaking. He spent the whole day lying, perhaps, not sleeping but that was the only option he had. His mother really endeavoured to keep him neat. He lied side by side with our aged, sick father under a shade in front of the house. Sometimes he’s being mistaken for the father.
Life became so terrible for him and to us he was staying with. I continued to offer the minimum assistance I could especially to the kids or through them.
Weeks went bye. I began to lose hope in his recovery.
Everyone in the village was refusing to talk on the sickness in our (relatives) presence. So did I. One day I was lying down with my wife late at night discussing the sickness. She mentioned that people in the village were suspecting that he was suffering from HIV/AIDS, so everyone was just waiting for his death. That was the end of our discussion that night. I refuse to comment on that suspicion.
I began to phone our other kins that they must come home and see him because he was dying. When we had a full house it was agreed that he be taken back to hospital. The doctor recommended three pints of blood immediately before any further treatment. We settled the bill and came back home, all of us hiding what many believe he was really suffering from.
The third pint could not get into him the second day … and he died.